Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Breaking News:

latest

Masar Da Najeriya Sun Fara Tattaunawa Kan Bunƙasa Koyar da Al-Ƙur’ani

Daraktan makarantar Nuri-Tilawah International School Zaria, Sheikh Dr. Nuruddeen Umar Tahir, ya jaddada buƙatar ƙarfafa...

Daraktan makarantar Nuri-Tilawah International School Zaria, Sheikh Dr. Nuruddeen Umar Tahir, ya jaddada buƙatar ƙarfafa haɗin gwiwar ƙasashen duniya domin inganta ilimin Al-Ƙur’ani, yana mai cewa hakan na da muhimmanci wajen tarbiyyar al’ummar Musulmi masu nagarta da ilimi.

Sheikh Tahir ya bayyana hakan ne a ranar Talata, 10 ga Fabrairu, 2026, yayin wata ziyarar aiki da ya kai ofishin Babban Mai ba da Fatawah na Jamhuriyar Larabawa ta Masar, Mai Alfarma Farfesa Sheikh Nazir Muhammad Ayyad, a hedikwatar Darul Ifta’i da ke birnin Alƙahira.

Da yake jawabi a yayin ganawar, Sheikh Dr. Nuruddeen Umar Tahir ya nuna godiya ga jagoran addinin na Masar bisa karɓar baƙuncinsa, yana mai cewa ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa wajen koyar da Al-Ƙur’ani a Najeriya, Afirka da kuma duniya baki ɗaya.

Ya bayyana cewa makarantar Nuri-Tilawah International School na da ƙudurin tarbiyyar ɗalibai da ba kawai za su haddace Al-Ƙur’ani ba, har ma su fahimci koyarwarsa tare da aiwatar da ita a rayuwarsu ta yau da kullum. Ya ƙara da cewa haɗin gwiwa da manyan cibiyoyin addini na duniya zai taimaka wajen inganta tsarin koyarwa, horar da malamai, tsara manhajar karatu da kuma bunƙasa bincike a fannin karatun Al-Ƙur’ani.


Sheikh Tahir ya kuma bayyana cewa karuwar buƙatar ilimin Al-Ƙur’ani a Najeriya da Afirka na buƙatar ƙarin haɗin gwiwa tsakanin cibiyoyin ilimi domin tallafa wa sabbin hanyoyin koyarwa tare da kiyaye sahihin tsarin karatu da tilawar Al-Ƙur’ani. Ya nuna fatan cewa wannan tattaunawa da Darul Ifta’i za ta buɗe sabbin hanyoyi na musayar ilimi da ƙwarewa ga malamai da ɗalibai.

A nasa jawabin, Babban Mufti na Masar, Farfesa Sheikh Nazir Muhammad Ayyad, ya yaba da ƙoƙarin makarantun Al-Ƙur’ani a Najeriya, yana mai bayyana rawar da suke takawa a matsayin muhimmi wajen kiyaye ilimin addinin Musulunci da kyawawan dabi’u.

Farfesa Ayyad ya bayyana cewa ilimin Al-Ƙur’ani shi ne ginshiƙin wayewar Musulunci, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin malamai da cibiyoyin ilimin addini a duniya. Ya kuma tabbatar da cewa Darul Ifta’i a shirye take ta tallafa wa shirye-shirye da ke inganta sahihin ilimin Musulunci da koyar da Al-Ƙur’ani, musamman a Nahiyar Afirka inda sha’awar ilimin addini ke ƙaruwa.

No comments